Rundunar sojin Najeriya ta bayyana cewa dakarun Operation HADIN KAI sun kama wani ɗan ƙasar Sudan, Musa Fashir mai shekaru 32, da ake zargi da kasancewa mayaƙin ta’addanci na ƙasashen waje.
A cewar rundunar, an kama wanda ake zargin ne a ranar 19 ga Yuli, 2026, yayin wani samame da aka kai a yankin Lassa da ke ƙaramar hukumar Askira/Uba ta jihar Borno, bayan samun bayanan sirri.
Rundunar ta ce binciken farko ya nuna cewa wanda ake zargin na da alaƙa da wasu ƙungiyoyin masu tayar da ƙayar baya, lamarin da ke nuna yiwuwar samun goyon baya daga wasu ‘yan ƙasashen waje ga ayyukan ta’addanci a Arewa maso Gabas.
Haka kuma, dakarun sun kama Mary Florence mai shekaru 36, wadda ta ce ‘yar ƙasar Ghana ce kuma ta shiga Najeriya ba bisa ƙa’ida ba.
Rundunar ta ce mutanen biyu na ci gaba da kasancewa a tsare yayin da ake gudanar da bincike domin tantance asalinsu da kuma yiwuwar alaƙarsu da ƙungiyoyin ta’addanci ko wasu laifukan ƙetare.
Sojoji Sun Kama Ɗan Sudan Da Wata ‘Yar Ghana Da Ke Da Alaƙa Da Ƴanta’adda A Borno

