Sojoji Sun Halaka Mayaƙan ISWAP Da Dama A Tafkin Chadi



Sojojin rundunar Operation HADIN KAI a Arewa maso Gabas sun lalata hanyoyin sufuri na kungiyar ISWAP tare da kashe ‘yan ta’adda da dama a yankin Tafkin Chadi kusa da tsibirin Kaniram a Jihar Borno.

Rahotanni sun nuna cewa sojojin sun kai hare-haren sama ne bayan samun bayanan sirri kan taruwar jiragen ruwa fiye da 30 na ‘yan ta’addan a yankin.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar, Laftanar Kanal Sani Uba, ya tabbatar da cewa an kai hare-haren ne bayan tantance wuraren da ake son kai hari.

A cewarsa, hare-haren sun lalata jiragen ruwa da kuma hana ‘yan ta’addan ci gaba da gudanar da ayyukansu, inda aka kashe sama da 30 daga cikinsu.

A wani hari dabam a yankin Sambisa, sojojin sun lalata motocin yaki guda uku tare da kashe wasu ‘yan ta’adda.

Rundunar ta ce har yanzu tana ci gaba da kai hare-hare domin murkushe ragowar ‘yan ta’addan a yankin.

More from this stream

Recomended