Sojoji Sun HaIIaka Ƴan Tq’qdda Uku A Zamfara



Dakarun rundunar Operation FANSAN YAMMA sun kashe ƴan ta’adda uku tare da ƙwato makamai da alburusai a jihar Zamfara.

Rahoton kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) ya ce sojojin sun gudanar da sintiri ne a ƙaramar hukumar Birnin Magaji, inda suka bi ta ƙauyukan Birnin Tsaba da Tsanu zuwa Dumburum.

Rahoton ya bayyana cewa an yi artabu da ƴan ta’addar a ƙauyen Dumburum, inda sojojin suka kashe mutum uku daga cikinsu tare da ƙwato bindigar AK-47 guda ɗaya, bindigar SK-21 A1, da wasu mujallu da alburusai masu yawa.

An kuma ce babu wani soja da ya rasa ransa ko ya jikkata yayin farmakin.

More from this stream

Recomended