
Shugaban jam’iyar APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda na cigaba da tattaunawa da yan jam’iyar adawa da suka fito daga Kano a ƙoƙarin da jam’iyar take na lashe zaɓen shekarar 2027.
Tsohon sanata Kabiru Ibrahim Gaya na daga cikin mutum na bayan-bayan nan da shugaban ya ziyarta a gidansa dake Abuja.
Sanata ya kasance jigo a jam’iyyar APC amma a yan kwanakin baya ya fice daga jam’iyyar inda ya koma jam’iyar adawa ta NDC.
Da yake jawabi kan ziyarar a cikin wani sako da ya wallafa, Nentawe ya ce ganawar ta gudana yadda ya kamata kuma ta mayar da hankali kan haɗa kan ƴan siyasar jihar Kano wuri guda.
Ganawar ta su na zuwa ne yan kwanaki kaɗan bayan da shugaban ya gana har sau biyu da, Rufa’i Sani Hanga sanata ɗaya tilo na jam’iyar NDC daga jihar Kano.

