Shin ko Najeriya ta mika kai ga Amurka kan mazambata? | BBC Hausa

Donald Trump

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Wasu daga cikin wadanda ake zargi suna zaune ne a Najeriya

Shugabar hukumar kula da ‘yan Najeriya mazauna kasashen waje, Abike Dabiri-Erewa, ta ce Najeriya za ta bai wa Amurka hadin kai wajen tuhumar wasu ‘yan Najeriya wadanda ake zargi da zamba ta hanyar intanet.

Ta bayyana hakan ne a wata hira ta musamman da sashen Hausa na BBC, inda ta kara da cewa ya kamata wadanda suka san suna da hannu su mika kansu ga hukumomi.

“Wadanda ke zaune a nan (Najeriya) kuma suka san suna da hannu gara ma su mika kansu, idan ba haka ba kuma za mu yi amfani da dokokin kasa-da-kasa kuma dole ne a mika su ga Amurka,” in ji Abike Dabiri.

A cikin makon nan ne dai rahotonni suka ambato ma’aikatar shari’a ta Amurka ta tuhumi mutum 80 akasarinsu ‘yan Najeriya bisa hannu kan wani gagarumin shirin hada baki don satar miliyoyin dala ta hanyar aikata damfara.

Wata sanarwa da ofishin babban lauyan gwamnatin Amurka wato atoni janar ya wallafa a shafin intanet ta bayyana tuhuma 252 da aka yi wa mutanen da ake zargi.

  • Cikin Hotuna: Abin da ya faru a Afirka makon nan
  • Madrid na fargaba kan lafiyar Neymar

Mutanen suna aiki da wani gungun masu halasta kudin haram da ke da sansani a birnin Los Angeles, in ji sanarwar.

Hukumar ta ce an gabatar da tuhume-tuhumen ne bayan jami’an tsaro a safiyar Alhamis sun kama mutum 14 a fadin Amurka, 11 daga cikinsu a birnin Los Angeles.

Biyu daga cikin wadanda ake zargin dama suna hannun hukumomi bisa wasu zarge-zargen na daban,inda kuma aka kama daya daga cikinsu a farkon makon nan.

Sauran wadanda ake zargin na zama ne a kasashen ketare, kuma yawancinsu na zaune ne a Najeriya.

“Kawo yanzu kotu ba ta same su da laifi ba amma muna so a yi shari’a ta adalci. Najeriya za ta bai wa Amurka hadin kai,” Abike Dabiri ta ce.

Ta kara da cewa: “Wannan ne ya sa muke kira ga ‘yan Najeriya da su kasance na gari a duk inda suke saboda indai ka yi laifi dole ne a hukunta ka.

“To amma fa bai kamata a yi mana kudin goro ba, a kyamace mu a matsayinmu na kasa ko al’umma. Idan mutane kalilan suka aikata laifi sai su dandana kudarsu.

“Amma mu ba haka muke ba a matsayinmu na ‘yan Najeriya.”

Tuhuma

Zarge-zargen da ake masu sun hada da cewa mutanen guda 80 da wasu da ke da alaka da su suna amfani da hanyoyin damfara daban-daban.

Hanyoyin da suka hada da tura sakonnin email da sunan kasuwanci da na soyayya da kuma wadanda ake tura wa tsofaffi, inda sukan damfari mutane miliyoyin dala.

Bayanan da gwamnatin ta Amurka ta gabatar a gaban kotu sun nuna cewa mazauna Amurka daga cikin wadanda ake zargi da yin damfarar su ne kan karbi miliyoyin dala daga wadanda suka damfara.

Daga nan kuma sai su tura kudaden zuwa abokansu cikin wannan sana’a da ke zaune a Najeriya da kuma wasu kasashen.

Bayanin ya kara da cewa mutum biyu daga cikin wadanda aka kama din na da hannu wajen tura kudi akalla dala miliyan 6, wadanda ake zargin an same su ne ta hanyar damfara.

Sannan kuma ana zargin cewa idan aka hada da sauran wadanda ke cikin wannan harka, sun yi yunkurin damfarar mutane kudi da suka kai dala miliyan 40.

Bayanin ya kara da cewa wadannan mutane kan damfari al’umma ne mazauna Amurka da ma fadin duniya baki daya.

Wadanda suka hada da kamfanoni manya da kanana da kuma tsofaffin mutane da dama.

Babban alkali na yankin California, Nick Hanna ya ce wannan shari’a wani yunkuri ne na kare Amurkawa daga masu damfara ta shafukan intanet da kuma tabbatar da cewa wadanda aka kama da irin wannan laifi sun fuskanci shari’a.

More News

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Gidaje 8925

Gwamnatin tarayya ta ce ta fara raba gidaje 8925  ga mutanen da suka nema kuma suka cancanci a basu a faɗin ƙasa baki ɗaya...

Ƴan Bindiga A Zamfara Sun Kashe Sakataren Jam’iyar PDP

Wasu ƴan bindiga da ba a san ko suwaye ba sun kashe, Musa Ille  sakataren jam'iyar PDP na ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara. Zagazola...