Sabon salon hana satar amsa ya yanjo rudani a kasar Indiya

ANI

Hakkin mallakar hoto
ANI

Wani jami’in wata makaranta a Indiya ya bayar da hakuri, bayan da wasu hotuna na wasu dalibai da suka rufe kawunansu da kwalaye yayin jarabawa ya rinka yawo a shafukan sada zumunta.

An dauki hoton ne a lokacin wata jarabawa a wata makarantar sharar fagen shiga jami’a ta Haveri da ke jihar Karnataka a Indiya.

Hotunan sun nuna daliban makarantar zaune a cikin aji da kwalaye bisa kawunansu, an huda kwalayen ta yadda za su samu iska.

An bayyana cewa an yi hakane domin hana daliban satar amsa.

Daya daga cikin malaman makaranatar ya fito ya roki gafara bayan afkuwar lamarin.

Ya ce makarantar ta yi amfani da wannan sabon tsarin ne sakamakon ta ji labarin tsarin ya yi amfani matuka a wata makarantar.

Ya kuma bayyana cewa an yi hakan ne da yardar daliban, kuma wasu daliban ma daga gidajensu suka zo da kwalayensu.

Ya ce ”ba a tilasta wa kowane dalibi da cewa dole sa ya saka kwali a kai ba, idan za ku iya gani akwai wadanda babu kwalin a kansu .”

Hakkin mallakar hoto
ANI

Ya ce ”wasu sun cire kwalayen bayan mintuna 15 wasu kuma bayan mintuna 20, bayan sa’a daya mu da kanmu muka ce kowa ya cire kwalin.”

Rahotanni sun bayyana cewa jami’ai a yankin sun garzaya makarantar bayan sun samu labarin wannan sabon tsarin da makarantar ta bullo da shi.

SC Peerjade wanda jami’i ne a kasar ya bayyana wannan sabon tsarin da makarantar ta yi gwaji a matsayin ”rashin imani.”

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...