Rikicin ADC: Bangaren David Mark Ya Zargi Nafiu Bala Da Kokarin Juya Kotu Zuwa “Kasuwanci”



Bangaren jam’iyyar ADC ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark, ya zargi Nafiu Bala da ƙoƙarin yin tasiri a harkar shari’a bayan kotun tarayya da ke Abuja ta ɗage shari’ar rikicin shugabancin jam’iyyar ba tare da sanya sabuwar rana ba.

Nafiu Bala, tsohon mataimakin shugaban jam’iyyar na ƙasa, ya kai ƙara yana ƙalubalantar shugabancin David Mark.

A zaman kotun, lauyan Bala ya bayyana cewa an rubuta wasiƙa zuwa ga babban alkalin kotun tarayya domin neman a mayar da shari’ar hannun wani alkali daban.

Alkalin da ke sauraron ƙarar, Emeka Nwite, ya ce ba zai iya yanke hukunci kan batun ba tare da sauraron ɓangarorin shari’ar ba, sannan ya ɗage sauraron ƙarar ba tare da sanya rana ba.

Da yake martani, kakakin ADC na ƙasa, Bolaji Abdullahi, ya ce wasu mutane na ƙoƙarin yin tasiri a harkar shari’ar domin canja alkali.

Abdullahi ya kuma ce jam’iyyar za ta ci gaba da mutunta doka, amma ba za ta amince da katsalandan a harkar shari’a ba.

More from this stream

Recomended