Ranar ma’aikata: Gwamnati ya ayyana Litinin a matsayin ranar hutu

An ayyana ranar Litinin 1 ga watan Mayu a matsayin ranar hutu domin bikin ranar ma’aikata ta bana.

Ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a.

Aregbesola, a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun babban sakataren ma’aikatar harkokin cikin gida, Shuaib Belgore, a ranar Juma’a, ya yabawa ma’aikatan Najeriya bisa kwazonsu da sadaukarwarsu.

Ya kara da cewa kokarin da ma’aikata ke yi shi ne ke da alhakin daukakar kasar da kuma mutunta Najeriya a yanzu a cikin kasashen duniya.

“Akwai mutunci a cikin aiki; dole ne mu himmatu da jajircewa kan aikin da muke yi domin yana da muhimmanci ga gina kasa,” inji shi.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]