Ranar ma’aikata: Gwamnati ya ayyana Litinin a matsayin ranar hutu

An ayyana ranar Litinin 1 ga watan Mayu a matsayin ranar hutu domin bikin ranar ma’aikata ta bana.

Ministan harkokin cikin gida, Rauf Aregbesola ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a.

Aregbesola, a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun babban sakataren ma’aikatar harkokin cikin gida, Shuaib Belgore, a ranar Juma’a, ya yabawa ma’aikatan Najeriya bisa kwazonsu da sadaukarwarsu.

Ya kara da cewa kokarin da ma’aikata ke yi shi ne ke da alhakin daukakar kasar da kuma mutunta Najeriya a yanzu a cikin kasashen duniya.

“Akwai mutunci a cikin aiki; dole ne mu himmatu da jajircewa kan aikin da muke yi domin yana da muhimmanci ga gina kasa,” inji shi.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]