Rahoto Ya Nuna Cewa Amurka Na Shirin Komawa Tattaunawa Da Iran A Pakistan

Kafar yaɗa labarai ta CBS ta ruwaito cewa jami’an Amurka na iya komawa Pakistan cikin ƴan kwanaki masu zuwa domin faɗaɗa tattaunawa da Iran.

Rahoton, wanda ya ambato wasu “majiyoyi masu alaƙa da tattaunawar”, ya ce gwamnatin Donald Trump na duba yiwuwar aika manyan jami’anta zuwa Pakistan don sake farfaɗo da shawarwarin diflomasiyya da Iran.

Sannan akwai yiwuwar a koma kan teburin tattaunawa a ranar Litinin mai zuwa.

A makon da ya gabata ne aka gudanar da wata tattaunawa a birnin Islamabad na Pakistan kan cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Iran da Amurka, sai dai ba a kai ga nasara ba.

Haka kuma, akwai rahotannin da ke cewa babban hafsan sojin Pakistan ya gana da jami’an Iran a birnin Tehran a ranar Alhamis, a wani yunƙuri na tsawaita wa’adin tsagaita wuta na wucin gadi.

More from this stream

Recomended