Oyedepo Ya Bukaci Mambobin Cocinsa Su Mallaki Katin Zaɓe



Jagoran Cocin Living Faith Worldwide, Bishop David Oyedepo, ya yi kira ga mambobin cocinsa da su mallaki katin zaɓe tare da shiga zaɓe domin cika hakkinsu na ‘yan ƙasa.

Oyedepo ya bayyana hakan ne a lokacin ibadar ranar Lahadi a Faith Tabernacle da ke Ota, Jihar Ogun.

Malamin cocin ya ce Kiristoci suna da alhakin taka rawa wajen zaɓen shugabannin ƙasashensu, yana mai jaddada cewa su cikakkun ‘yan ƙasa ne, don haka bai kamata su kauce wa tsarin dimokuraɗiyya ba.

Ya kuma ce kasancewar cocin na da miliyoyin mambobi a faɗin duniya, hakan ya ba ta damar taka muhimmiyar rawa a harkokin ƙasashe ta hanyar sahihin zaɓe.

More from this stream

Recomended