Okowa ya ziyarci ofishin EFCC dake Lagos

Tsohon gwamnan jihar Delta, Ifeanyi Okowa ya ziyarci ofishin hukumar EFCC dake jihar Lagos a ranar Litinin.

Wasu majiyoyi dake hukumar ta EFCC sun bayyana cewa ziyarar ta tsohon gwamnan na da alaƙa  da binciken almundahanar kuɗaɗe da ake zargin ya aikata lokacin da yake jagorantar jihar Delta.

A watan Nuwamban shekarar 2024 ne hukumar yaki da cin hanci da rashawar ta kama Okowa inda ta zarge shi da karkatar da kudade har naira tiriliyan ɗaya da biliyan ɗari uku a tsahon shekaru 8 da ya shafe yana mulkar jihar Delta.

An kuma zarge shi da yin amfani da dukiyar al’umma wajen mallakar gine-gine a biranen Abuja da kuma Asaba babban birnin jihar.

Da yake magana bayan kama shi tsohon gwamna ya ce anyi amfani da kuɗaɗen jihar bisa ka’ida ta yadda ya kamata a lokacin mulkinsa inda ya ƙara da cewa baya tsoron bincike.

More from this stream

Recomended