NDLEA ta kama wasu dattawa dake sayarwa da daliban sakandare miyagun kwayoyi

Hukumar NDLEA dake yaki da hana sha da fataucin miyagun kwayoyi ta samu nasarar kama wasu dattawa biyu da ake zarginsu da sayarwa ɗaliban sakandare ƙwaya.

An bayyana mutanen da aka kama da suna, Godfrey Orji mai shekaru 82 da kuma Godwin Obolunbiya Obiora kuma  an kama su ne a wani samame da aka kai a lokuta daban-daban a Umuahia babban birnin jihar dai-dai lokacin da hukumar ke cigaba da ƙoƙarin kawo karshe miyagun kwayoyi a jihar.

Femi Baba Femi mai magana da yawun hukumar a cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi ya ce an kama Obiora ne a ranar 19 ga watan Yuni biyo bayan sirri da aka samu kansa da ya nuna cewa yana amfani da shagonsa na magani dake kan titin Club wajen sayar da haramtattun kayan maye ga yara ɗalibai yan sakandare.

Binciken da hukumar ta yi a shagonsa ta gano ƙwayar Tramadol da Diezapam mai nuyin kilogiram 4.64.

Babafemi ya ce Orji wanda ɗan fansho ne am kama shi ne  ranar 18 ga watan Yuni bayan da maigadi a  makarantar sakandaren Saint Silas da ke Umuahia a dai-dai lokacin da yake bawa wasu dalibai kayan maye su sayar masa.

More from this stream

Recomended