Najeriya za ta kasance kasa ta biyu a duniya da ta fi shigo da shinkafa

Ma’aikatar noma ta Amurka ta yi hasashen cewa Najeriya za ta kasance kasa ta biyu a fadin duniya da tafi sayan shinkafa daga kasashen waje.

Hasashen ya nuna cewa kasar China za ta kasance kasa ta farko da za tafi shigar da shinkafa cikin kasar daga ƙasashen waje.

“China da Najeriya za su cigaba da kasancewa wadanda suka fi shigo da shinkafa a shekarar 2019 ya yin da Tarayyar Turai ke bi musu baya sai kuma kasashen Cote di’ voire da Iran .”a cewar hasashen.

Tun da fari ministan harkokin noma na Najeriya, Audu Ogbeh ya yi gargadin cewa kasar na iya fuskantar karancin shinkafa a shekarar 2019 idan har ba a dauki matakai ba biyo bayan ambaliyar ruwa da aka samu a wasu jihohin.

Gwamnatin shugaban kasa, Muhammad Buhari ta ci alwashin kawo karshen dogaro da kasashen waje da Najeriya ta yi wajen samun shinkafar da take bukata

More News

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...