Najeriya za ta kasance kasa ta biyu a duniya da ta fi shigo da shinkafa

Ma’aikatar noma ta Amurka ta yi hasashen cewa Najeriya za ta kasance kasa ta biyu a fadin duniya da tafi sayan shinkafa daga kasashen waje.

Hasashen ya nuna cewa kasar China za ta kasance kasa ta farko da za tafi shigar da shinkafa cikin kasar daga ƙasashen waje.

“China da Najeriya za su cigaba da kasancewa wadanda suka fi shigo da shinkafa a shekarar 2019 ya yin da Tarayyar Turai ke bi musu baya sai kuma kasashen Cote di’ voire da Iran .”a cewar hasashen.

Tun da fari ministan harkokin noma na Najeriya, Audu Ogbeh ya yi gargadin cewa kasar na iya fuskantar karancin shinkafa a shekarar 2019 idan har ba a dauki matakai ba biyo bayan ambaliyar ruwa da aka samu a wasu jihohin.

Gwamnatin shugaban kasa, Muhammad Buhari ta ci alwashin kawo karshen dogaro da kasashen waje da Najeriya ta yi wajen samun shinkafar da take bukata

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]