Ƙungiyar likitoci ta Médecins Sans Frontières (MSF) ta ce ana ci gaba da samun ƙaruwar yaran da ke fama da rashin abinci mai gina jiki a jihar Kebbi da ke Arewa maso Yammacin Najeriya.
Ƙungiyar ta bayyana cewa matsalar tamowa na barazana ga rayuwar yara ƙanana a jihar da ma sauran yankin arewa maso yamma.
A wata sanarwa da ta fitar, MSF ta ce ta lura da ƙaruwa mai yawa na masu fama da matsanancin rashin abinci mai gina jiki tsakanin shekarun dubu biyu da ashirin da huɗu zuwa dubu biyu da ashirin da biyar. Ta ce hakan ya sa ta sauya dabarun agaji domin dakile matsalar kafin ta janyo asarar rayuka masu yawa.
MSF ta ce alƙaluman UNICEF sun nuna cewa ana rasa kusan yara talatin cikin ɗari masu ƙasa da shekara biyar a kowace rana saboda matsalolin da ke da alaƙa da tamowa, kuma kusan rabin mace-macen na faruwa ne a jihar Kebbi.
Shugaban MSF a Najeriya, Stuart Alexander Zimble, ya ce, “Rashin abinci mai gina jiki ya yi tsanani matuƙa a jihar Kebbi kuma yana daga cikin manyan abubuwan da ke haddasa mutuwar jarirai da ƙananan yara ƴan ƙasa da shekara biyar.”
MSF Ta Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Tamowa A Kebbi

