Mayakan jihadi sun kashe ma′aikatan sa kai Burkina Faso

Harin ya auku ne a lokacin da ma’aikatan ke aikin tsaro na sinitiri a yanjkin arewacin kasar.

Maikatan sun bi sahun wasu barayi dabbobi ne da suka yi awon gaba da busashe a lokacin da ‘yan bindigar suka hallakasu a Siguidi kusa da lardin Gorasdi

A shakarar 2019 ne aka kafa wannan kungiya ta VDP da zummar taimakawa jami’an soji yaki da mayakan da ke gwagwarmaya da makamai, amma suna fama da munanan hare-hare a lokuta da dama wanda tun daga shekara bara kawo yanzu aka kashe sama da mutum 200 daga cikinsu.

Ire-iren wadannan hare-haren a kan farafen hula da masu bada agaji na kara karuwa a koda yaushe wanda a ‘yan kwanakin nan, Majalisar Dinkin Duniya ta sanar da kwashe ma’aikatanta daga shiyar arewa maso gabashin Najeriya bayan wani hari a offishinsu.

More News

Ƴan Fashin Daji Sun Kashe Mutane 7 A Jihar Kebbi

Mutane 7 aka bada rahoton ƴan fashin daji sun kashe  a garin Tudun Bici dake ƙaramar hukumar Danko Wasagu ta jihar Kebbi. A cewar mazauna...

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraɗiyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...