Mayakan jihadi sun kashe ma′aikatan sa kai Burkina Faso

Harin ya auku ne a lokacin da ma’aikatan ke aikin tsaro na sinitiri a yanjkin arewacin kasar.

Maikatan sun bi sahun wasu barayi dabbobi ne da suka yi awon gaba da busashe a lokacin da ‘yan bindigar suka hallakasu a Siguidi kusa da lardin Gorasdi

A shakarar 2019 ne aka kafa wannan kungiya ta VDP da zummar taimakawa jami’an soji yaki da mayakan da ke gwagwarmaya da makamai, amma suna fama da munanan hare-hare a lokuta da dama wanda tun daga shekara bara kawo yanzu aka kashe sama da mutum 200 daga cikinsu.

Ire-iren wadannan hare-haren a kan farafen hula da masu bada agaji na kara karuwa a koda yaushe wanda a ‘yan kwanakin nan, Majalisar Dinkin Duniya ta sanar da kwashe ma’aikatanta daga shiyar arewa maso gabashin Najeriya bayan wani hari a offishinsu.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]