Kana da labarin Rahaf Mohammed, wacce ta yi RIDDA sannan ta tsere wa ‘yan’uwanta?, Daga Muhammadu Sabiu

 

Wannan ita ce Rahaf Mohammed, budurwa ‘yar shekara 18 kuma ‘yar asalin k’asar Saudiyya da yanzu ta samu mafaka a k’asar Canada bayan ta tsere wa ‘yan’uwanta lokacin da suka je hutu a k’asar Kuwait.

Ta tsere ne kuwa ba don komai ba sai don RIDDA da ta yi, wanda laifi ne da hukuncinsa kisa ne a k’asashe irin su Saudiyya – inda ba a wasa da Shari’ar Musulunci. A cewarta, ana danne mata hakkokinta na ‘ya mace kuma tana matuk’kar fuskantar barazana sakamakon barin Musulunci da ta yi da kuma rashin amincewarta da wani auren zumunci da za a yi mata.

Bayan barinta Kuwait, ba ta tsaya a ko’ina ba sai a Birnin Bangkok na k’asar Thailand, inda daga nan ne ta yi niyyar cillawa Australia don neman mafaka. To sai dai hakan ya ci tura. A daidai wannan lokaci ne mahukuntan k’asar Thailand suka sassauta dokokinsu na ‘yan gudun hijira, har suka k’i mayar da ita inda ta fito – wato Kuwait – kafin daga nan a mayar da ita Saudiyya.

A bangkok ne ta samu kulawar Majalisar D’inkin Duniya har ta samu nasarar karb’uwa a k’asar Canada.

“…ni ce Rahaf Mohmed [sic], wacce nake neman mafaka a duk k’asar da za ta kare ni daga illa ko kisa da ‘yan’uwana za su min saboda na yi
Ridda,” a cewar Rahaf.

Allah sarki Rahaf! Allah Ya sa ki gane!

Muhammadu Sabiu ne ya rubuta wannan makala. Za a iya samunsa ta kafar Facebook: Muhammadu Sabiu

More from this stream

Recomended

Mutane 7 Sun Rasa Rqyukansu, 53 Sun Jikkata Sakamakon Guguwar Iska a Jigawa

Akalla mutane bakwai sun rasa rayukansu, yayin da 53 suka jikkata bayan wata guguwar iska ta yi barna a kananan hukumomi 13 na jihar Jigawa. Rahotanni sun nuna cewa guguwar ta shafi gidaje 5,403 a cikin garuruwa 120, inda ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu, gidajen zama da sauran […]