Mayaƙan Boko Haram Biyu Sun Miƙa Kansu Ga Sojoji

Aƙalla mayaƙan Boko Haram biyu ne suka miƙa kansu ga dakarun sojan Najeriya na rundunar Operation Haɗin Kai a yankin gabashin jihar Borno.

Mayaƙan biyu Awana Malam Kurama da Tahir Isa sun miƙa kansu ne ga sojojin rundunar Operation Haɗin Kai dake Bama bayan da suka  gudo daga sansaninsu dake ƙauyen Bahrain a Dajin Sambisa ranar 8 ga watan Mayu.

Wasu majiyoyin jami’an tsaro sun faɗawa Zagazola Makama dake wallafa bayanai kan sha’anin tsaro a yankin tafkin Chadi cewa mayaƙan biyu sun miƙawa jami’an tsaro bindiga guda ɗaya ƙirar AK-47 da harsashi guda 10 kuɗi ₦29,000 da kuma kekuna guda biyu.

Jami’an soja na cigaba da tsare mutanen inda ake cigaba da ɗaukar bayanansu.

More News

An sanar da zaman makoki na kwana biyar saboda mutuwar shugaban kasa a Iran

Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya sanar da zaman makoki na kwanaki biyar saboda rasuwar shugaban kasar Ibrahim Raisi...

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa ɗaya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faɗa tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...