Matashi ya mayar da naira miliyan 15 wa fasinjan da ya manta su a a-daidaita-sahunsa

Wani matashi mai suna Auwalu Salisu dan shekara 22, ya mayar da naira miliyan 15 da wani fasinja ya manta da shi.

Fasinjan dai ya zo ne daga kasar Chadi don sayen kaya a Kano sai kuma ya manta da shi.

Salisu wani mazaunin Yankaba da ke karamar hukumar Nasarawa a cikin babban birnin jihar, ya mayar da kudin ne bayan ya ji sakon bacewar kudin a wani gidan rediyo da ke Kano.

Kudaden wadanda sun kai maira miliyan 15 idan aka canza su, sun hada da; CFA miliyan 10.130 da kuma Naira miliyan 2.9.

Da yake zantawa da gidan rediyon Arewa a Kano, ya ce bai lura fasinjan nasa ya manta da kudin ba har ya isa gida.

Ya ce bayan gano kudin ne ya sanar da iyayensa wadanda suka umarce shi da ya je ya nemo mai shi.

More News

An samu ambaliyar ruwa a Adamawa

Anguwan Tana, al’ummar karamar hukumar Yola ta Arewa, sun shiga tasgaro a ranar Alhamis sakamakon ambaliya daga kogin Kilange da kogin Faro. Mazaunan garin...

Sojoji sun ceto mutane 6 daga cikin É—aliban jami’ar Gusau da aka sace

Sojoji sun ceto dalibai mata shida daga cikin daliban Jami'ar Gwamnatin Tarayya dake Gusau da aka bada rahoton yan bindiga sun yi garkuwa da...

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da É—aliban Jami’ar Tarayya da ke Gusau

An sace wasu daliban jami’ar tarayya ta Gusau da ba a tantance adadinsu ba da sanyin safiyar Juma’a. ‘Yan ta’addan masu yawan gaske sun...

Ƴan sanda sun kama masu safarar makamai wa ƴan bindiga

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Karasuwa a jihar Yobe sun cafke wasu mutane biyu da ake zargi da kai wa ‘yan bindiga makamai da...