Manoman Diffa Sun Koka Kan Matsalolin Da Ke Barazana Ga Noma



Manoma a jihar Diffa da ke jamhuriyar Nijar sun bayyana damuwa kan matsalolin da ke barazana ga samar da abinci a yankin.

Sun ce rashin tsaro da hare-haren masu ɗauke da makamai, sauyin yanayi da kuma kwari masu lalata amfanin gona na daga cikin manyan ƙalubalen da suke fuskanta. A cewarsu, matsalolin sun haddasa ƙarancin kayan noma a kasuwanni tare da jefa manoma cikin mawuyacin hali.

Kokex-koken na zuwa ne yayin da ake shirin fara damina da kuma gyaran gonaki domin sabon kakar noma.

More from this stream

Recomended