Mahaifi ya fille kan ɗiyarsa don yin asiri

Jami’an tsaro na jihar Edo sun kama wani mutum mai suna Emmanuel Ovwarueso bisa zarginsa da fille kan diyarsa bisa zarginta da laifin kashe kudi a garin Benin na jihar Edo.

An kama wanda ake zargin ne a Uteh, Upper Mission, inda yake zaune a ranar Alhamis din da ta gabata da misalin tsakar dare tare da kam marigayiyar a cikin wata leda

An ce ya aikata wannan mummunan aiki, sai da ya daure matarsa inda ya aiwatar da kisan a gabanta.

Matarsa, wacce ba a bayyana sunanta ba a lokacin da aka buga wannan rahoton, ta ce, “Halin mijina ya canza kwanan nan.  Ya ci gaba da cewa kada in kara kallonsa a matsayin talaka.

“A wurin aikinsa yana siya wa kowa abin sha kamar yana bikin. Hatta abokan aikinsa sun yi mamakin sabon salon kashe kudinsa. 

“Har ya ce musu kudinsa na kusa.  Ba mu taba sanin yana da shirin yin amfani da ’yarmu wajen yin asiri ba.”

More News

Sojoji sun kashe kwamandojin ƴan ta’adda a Najeriya

Hedikwatar tsaro ta Najeriya ta ce bangarenta na rundunar Operation Hadin Kai a ranar 10 ga watan Janairu ya kawar da wasu manyan kwamandojin...

Wani ya kashe abokinsa saboda kuɗin farantin abinci

Wani mutum mai suna John ya rasa ransa bayan abokinsa, Akinola Adeleye, ya caka masa wuka har lahira a kan takaddamar wanda zai biya...

Matashi ya kashe kakarsa mai shekara 100 saboda ta ƙi mutuwa

A ranar Alhamis ne aka zargi wani mutum da kashe kakarsa mai shekaru 100 da gatari yayin da take zaune a kan keken guragu....

Ƴan sandan jihar Bauchi sun kama mutum 9 da ake zargi da fashi da makami

‘Yan sanda a jihar Bauchi sun yi nasarar cafke wasu mutane tara da ake zargi da aikata laifin fashi da makami da addabar mazauna...