Labarin wasanni: Madrid za ta musanya Bale da Pogba, Palace ba ta son sakin Zaha

Gareth Bale da Pogba

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

An dade ana hasashe kan makomar Bale da Pogba a Real Madrid da Manchester United

Real Madrid a shirye take ta bayar da Gareth Bale mai shekara 29 domin karbo Paul Pogba daga Manchester United mai shekara 26, in ji jaridar Mail.

Sai Manchester United ta biya fam miliyan 90 idan har tana son sayen Harry Maguire mai shekara 26 daga Leicester City – inda dan wasan na Ingila zai kasance dan wasan baya mafi tsada a tarihi, a cewar Telegraph.

Manchester United ta nuna sha’awar dan wasan Spain Dani Olmo da ke taka leda a Dinamo Zagreb mai shekara 21, in ji Daily Mail.

Crystal Palace ba ta son sayar wa Arsenal dan wasan Ivory Coast Wilfried Zaha, mai shekara 26, in ji Daily Mirror.

Akwai yiyuwar Alexandre Lacazette, mai shekara 28 zai bar Arsenal kafin rufe kasuwar musayar ‘yan wasa, a cewar Express.

Atletico Madrid na son dauko Lacazette domin maye gurbin Antoine Griezmann, mai shekara 28 idan ya koma Barcelona, in ji Daily Mirror.

Barcelona na jiran tayin dan wasanta na baya Samuel Umtiti, mai shekara 25, wanda Manchester United ke son saya, in ji Sport, via Mirror.

Dan wasan Faransa Ousmane Dembele, mai shekara 22, yana son ci gaba da taka leda a Barcelona duk da manyan kungiyoyi sun nuna suna sha’awarsa kamar Liverpool da Bayern Munich, a cewar jaridar L’Equipe.

Aston Villa tana son sayo dan wasan Kasimpasa dan kasar Masar Mahmoud Trezeguet, mai shekara 24, in ji jaridar Sun.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...