La Liga: Levente ta yi wa Barcelona mahangurba | BBC news

Lionel Messi

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Messi ne ya fara cin bugun finareti

Barcelona ta sha mamaki a wasan La Liga mako na 12 bayan Levente ta lallasa ta da ci 3-1 a filin wasa na Estadio Ciudad Valencia.

Messi ne dai ya fara tsokano tsuliyar dodon da kwallon da ya ci daga bugun finareti a minti na 38 kafin daga bisani Jose Campana ya farke ta farke a minti na 61.

Levente ta yi wa Barcelona rubdugu, inda ta ci kwallo biyu a cikin minti 10 ta hannun tsohon dan wasan Real Madrid Borja Mayoral da kuma Nemanja Radoja.

Sai dai tun a minti na 74 Messi ya kara ta biyu amma na’ura mai taimaka wa alkalin wasa ta VAR ta hana, inda ta ce an yi satar gida.

Wannan rashin nasarar ita ce ta uku a cikin wasa 11 da Barca ta buga a La Ligar bana kuma Real Madrid ka iya komawa saman teburi a daren yau.

Yanzu dai ta rikito daga mataki na daya zuwa na biyu da maki 22 a wasa 11, yayin da abokiyar hamayyarta Real Madrid za ta karbi bakuncin Real Betis da karfe 9:00 na daren yau Asabar.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...