Kun san wanda ya kirkiri kalmar Kannywood? | BBC Hausa

INSTAGRAM/@OFFICIAL_HAFSAIDRIS20
Hakkin mallakar hoto
INSTAGRAM/@OFFICIAL_HAFSAIDRIS20

Wani dan jarida kuma mai sharhi kan harkokin fina-finan Kannywood, Ibrahim Sheme ya ce kalmar ta Kannywood wadda aka samar da ita a 2002, ta samo asali ne daga Malam Sunusi Shehu Danejo, wani marubucin Hausa a jihar Kano da ke arewa maso yammacin Najeriya.

Sheme ya shaida wa BBC cewa Malam Shehu ya fara amfani da kalmar ta Kannywood cikin wata mujalla mai bayar da labaran fina-finan Hausa, mai suna Tauraruwa.

A cewar Sheme, “ni ma na bayar da gudummawa wajen kirkiro wannan kalma, a lokacin da Malam Sunusi ya kirkiro wannan kalma yana amfani da ‘N’ guda daya a cikin kalmar Kanny din.”

“Wato Kany ya rika amfani da ita. Da na ga yana amfani da kalmar Kannywood da ‘N’ guda daya, sai nake tunanin ba dai-dai ba ne,” in ji Sheme.

Ya kara da cewa asalin kalmar daga Hollywood aka dauko ta sannan “masu yin harkar fina-finai na kudancin Najeriya suna amfani da Nollywood.”

Sheme ya bayyana cewa a lokacin “na ga kamata ya yi a ce Kalliwood don haka sai na fara amfani da kalmar Kalliwood a cikin mujallar fim.”

Ya ce a wancan lokacin shi Malam Shehu yana amfani da Kanywood da N guda daya sai dai daga baya ne kuma ya gane cewa mutane sun fi sabawa da kalmar da shi Malam Shehun ya kirkiro ta Kanywood.

Ya ce “don haka sai na koma amfani da Kannywood amma kuma sai na ki amfani da tasa a yadda yake rubuta ta.”

“Sai na kara ‘N’ guda daya don ya zama Kannywood kamar yadda can yake Hollywood da Nollywood da ‘L’ guda biyu, toh sai naga ya kamata a rika amfani da N guda biyu.” kamar yadda Sheme ya ce.

Tuni dai wannan kalma ta zama shahararriya a yanzu, ta yadda har aka sanya ta a kamus din Turanci na Oxford da ake wallafawa a Birtaniya a baya-bayan nan.

More News

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...

Manyan dillalan mai za su fitar da litar man fetur miliyan 300 a wannan makon

Ƙungiyar MEMAN ta manyan dillalan man fetur da dangoginsa ta ce mambobinta sun fara lodin mai har lita miliyan 300 a cikin makon nan...

Kotu ta É—aure mutumin sa ya yi sama-da-faÉ—i da kuÉ—in marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...