Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta ba da umarnin ƙwace kadarori 48 da ake alaƙanta su da tsohon Babban Lauyan Tarayya kuma Ministan Shari’a, Abubakar Malami, tare da mayar da su mallakin Gwamnatin Tarayya.
Mai Shari’a Joyce Abdulmalik ta ce Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) ta gabatar da isassun hujjoji da suka nuna cewa kadarorin na da alaƙa da kuɗaɗen da ake zargin sun samo asali daga haramtattun ayyuka.
Kotun ta kuma yanke hukuncin cewa Malami, iyalansa da kamfanonin da ake alaƙanta da kadarorin ba su iya karyata zargin da EFCC ta gabatar ba.
Rahotanni sun nuna cewa kadarorin da aka ƙwace suna jihohin Abuja, Kano, Kebbi da Kaduna, yayin da Malami ke ci gaba da fuskantar shari’a kan zargin damfarar Naira biliyan 8.7 tare da matarsa da ɗansa.
Kotun Tarayya Ta Ba Da Umarnin Ƙwace Kadarori 48 Da Ake Alaƙanta Su Da Abubakar Malami

