Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Kisa A Kano


Kotun koli ta Jihar Kano ta yanke wa wani matashi mai suna Umar Idris hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan samunsa da laifin kisan wani dan kasuwa, Sabiu Umar.

Kotun ta bayyana cewa wanda ake tuhuma ya aikata laifin ne bayan ya shiga shagon mamacin da daddare ba tare da izini ba domin yin sata, inda rikici ya barke tsakaninsu.

Rahotanni sun nuna cewa a yayin rikicin, Umar Idris ya daba wa mamacin wuka a sassa daban-daban na jikinsa, lamarin da ya yi sanadin mutuwarsa.

Alkalin kotun, Mai shari’a Sunusi Ado-Ma’aji, ya ce an tabbatar da laifin ba tare da wata shakka ba, sannan ya yanke masa hukuncin kisa ta hanyar rataya.

More from this stream

Recomended