
Babbar Kotun Tarayya dake zamanta a birnin tarayya Abuja ta yanke wa mutane 4 hukunci a cikin mutane biyar da suka kai harin ta’addanci a wata coci dake garin Owo na jihar Ondo.
Mai shari’a, Emeka Nwite ne ya yanke wa mutanen huɗu hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan ya same su da aikata dukkanin laifuka 9 da ake tuhumarsu da aikatawa.
Waɗanda aka yankewa hukuncin kisa Idris Abdulmalik Omeiza (shekaru 25 ), Al Qasim Idris (shekaru 20 ), Jamiu Abdulmalik (shekaru 26 ) da kuma Abdulhaleem Idris (shekaru 25).
Mutum na biyar Momoh Otuho Abubakar mai shekaru 47 da ake tuhumarsu tare an wanke shi daga laifi kuma an sallame shi.
Masu ibada da basu gaza 41 ne ba aka kashe a yayin da aka jikkata wasu sama da 69 lokacin da yan bindiga su ka buɗe wuta da bindigu tare da jefa bama-bamai a cocin a ranar 22 ga watan Yuni na shekarar 2022.

