Kotu ta sauke gwamnan Filato daga kujerarsa

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta sauke gwamnan jihar Filato, Caleb Mutfwang, daga kujerarsa.

A hukuncin da ta yanke a ranar Lahadi, babbar mai shari’a Elfrieda Williams-Dawodu, ta umurci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) da ta ba dan takarar jam’iyyar All Progressives Congress, Nentawe Goshwe takardar shaidar cin zabe.

Mai shari’a Williams-Dawodu ya yi watsi da hukuncin kotun da ta tabbatar da zaben gwamna Mutfwang, inda ya bayyana shi a matsayin wanda bai dace ba.

Har yanzu dai Caleb Mutfwang yana da damar kara kai kara kotun koli idan yana tantamar wannan hukuncin.

More News

Ƴansanda sun hallaka masu garkuwa da mutane

Ƴansanda sun hallaka wasu masu garkuwa da mutane uku da ake zargin sun yi yunkurin yin garkuwa da matar wani dan majalisar dokokin jihar...

Ƴansanda a Katsina sun yi nasarar cafke wasu tantiran masu safarar alburusai wa ƴanbindiga

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Juma’a ta sanar da cewa ta kama wasu manyan ‘yan bindiga guda uku tare da kwato manyan...

Tinubu ya amince da mafi karancin albashi na N70,000

Shugaba Bola Tinubu ya amince da N70,000 a matsayin mafi karancin albashi ga ma’aikatan Najeriya, inda ya yi alkawarin sake duba dokar mafi karancin...

Mutanen Isra’ila sama da rabin miliyan sun tsere saboda yakin Gaza

Mutanen Isra'ila sama da rabin miliyan ɗaya ne suka fice daga ƙasar kuma ba su koma ba a watanni shida na farkon yaƙin Isra'ila...