Daruruwan ’yan Najeriya da suka nemi a dawo da su daga Afirka Ta Kudu bayan hare-haren ƙiyayya ga baƙi na fama da matsaloli sakamakon jinkirin jiragen kwaso da gwamnatin tarayya ta shirya.
Ƙungiyar ’Yan Najeriya a Afirka Ta Kudu (NICASA) ta bayyana cewa mutane da dama sun fito daga jihohi daban-daban domin yin rajista da tantancewa, amma yanzu sun rasa wajen kwana, abinci da kuɗin sufuri.
Tun a ranar bakwai ga watan Yuni ne gwamnatin tarayya ta sanar da shirin tura jiragen Air Peace guda biyar domin dawo da ’yan Najeriya. Sai dai kawo yanzu jirgi guda ne kawai ya iso Lagos da mutane dari biyu da hamsin da takwas, duk da cewa sama da mutane dubu ɗaya sun nuna sha’awar dawowa gida.
NICASA ta roƙi gwamnatin tarayya da sauran hukumomi su gaggauta kammala sauran jiragen kwaso tare da bayar da tallafin gaggawa ga mutanen da suka makale.
Mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Waje, Kimiebi Ebienfa, ya ce har yanzu babu sabon bayani kan aikin kwaso mutanen. Shi kuma jami’in hukumar NiDCOM, Abdur-Rahman Balogun, ya tabbatar da cewa duk wanda ya yi rajista za a dawo da shi gida, tare da roƙon mutane su yi haƙuri yayin da gwamnati ke ci gaba da aikin.
Ƴan Najeriya Sun Makale A Afirka Ta Kudu Saboda Jinkirin Jigilarsu Zuwa Gida

