Kotu Ta Yanke Wa Mahaifiya Da ’Yar Uwar Dan Ta’adda Battujo Hukuncin Shekaru Arba’in



Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yanke wa Safiya Salihu da Halima Abdullahi hukuncin zaman gidan yari bayan sun amsa laifukan da suka shafi ta’addanci.

Matan biyu mahaifiya da ’yar uwar marigayi Kachallah Ibrahim Battujo ne, wanda jami’an tsaro suka kashe a jihar Kogi a watan Yuni.

Mai shari’a Hauwa Yilwa ta yanke hukuncin ne bayan wadanda ake tuhuma sun amsa laifukan taimakawa ayyukan Battujo da kuma ɓoye bayanai game da harkokinsa.

Kotun ta wanke su daga wasu tuhume-tuhume biyu da suka shafi karɓar kuɗaɗen da ake zargin sun fito daga ayyukan ta’addanci da kuma tallafin zuwa aikin hajji.

An yanke wa kowacce daga cikinsu hukuncin daurin shekaru ashirin, wanda kotun ta ce za su yi lokaci guda. Haka kuma kotun ta umarci a yi musu gyaran hali bayan kammala zaman yarin.

More from this stream

Recomended