Babbar Kotun Babban Birnin Tarayya (FCT) ta ba tsohon gwamnan jihar Taraba, Darius Ishaku, izinin tafiya birnin Dubai domin duba lafiyarsa da kuma yi masa tiyata.
Mai shari’a Sylvanus Oriji ne ya amince da buƙatar a ranar Talata bayan lauyan Ishaku ya gabatar da ita, yayin da masu gabatar da ƙara ba su nuna adawa ba. Kotun ta kuma ɗage ci gaba da shari’ar zuwa ranar 5 Oktoba, 2026.
Ishaku da tsohon Babban Sakataren Ma’aikatar Ƙananan Hukumomi da Harkokin Masarautu ta jihar Taraba, Bello Yero, na fuskantar tuhuma 15 da suka haɗa da cin amanar gwamnati, haɗa baki da karkatar da kuɗaɗen jama’a. Sai dai dukkansu sun musanta zarge-zargen.
A ci gaba da shari’ar, wani shaida ya sake bayyana wa kotu yadda aka tura kuɗaɗe daga wasu ƙananan hukumomi zuwa asusun wani kamfani domin sayen kayan abincin Kirsimeti, tare da zargin cewa an aiwatar da hakan bisa umarnin Bello Yero.
Kotu Ta Ba Tsohon Gwamnan Taraba Izinin Tafiya Dubai Domin Jinya

