Kotu ta ɗaure mutumin sa ya yi sama-da-faɗi da kuɗin marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda samunsa da laifin wawure kuɗin marayu kimanin naira miliyan 12.

Hukumar EFCC ce ta wallafa bayanin ranar Talata shafinta na Twitter.

Tun a ranar 3 ga watan Yulin 2023 ne hukumar EFCC ta gurfanar da shi a gaban kotun kan zargin karkatar da dukiyoyin magada da aka ƙiyasta kuɗinsu ya kai kimanin naira miliyan 12 ga buƙatar kansa maimakon amfani da ita wajen kula da magada.

Dukiyoyin sun haɗa da gidaje uku da filaye biyu da aka kange – ɗaya daga ciki ɗauke da shaguna bakwai sai gidajen burodi biyu da wani fili da manyan tankoki biyu sai babban injin janareto.

More News

An fara rushe wasu gine-gine 500 a kasuwar Karmo dake Abuja

Hukumar FCTA dake kula da birnin tarayya Abuja ta fara rushe gine-gine sama da 500 da aka yi ba bisa ka'ida ba a kasuwar...

Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa

A ranar Alhamis ne shugaba Bola Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa, a ziyarar da Faye ya...

NEMA ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo dasu gida daga ƙasar Chad

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA ta ce ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo da su bayan da su ka maƙale...

Ƙungiyar ƙwadago ta ƙi amincewa da ₦48,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi

Taron zaman ganawa da ƴan kungiyar ƙwadago da gwamnatin ta tarayya ta kira  ya tashi babu shiri bayan da wakilan kungiyar ƙwadago suka fice...