Kotu a Kebbi Ta Ɗage Shari’ar Nas Da Ake Zargi Kan Mutuwar Yara Biyu

Babbar Kotun Jihar Kebbi ta ɗage sauraron shari’ar wata nas mai suna Hannatu James da ake tuhuma kan mutuwar wasu yara biyu a Asibitin Martha Bamaiyi da ke Zuru.

Mai shari’a Nusirat Ibrahim Umar ta ɗage karar zuwa ranar 13 ga watan Yulin 2026 bayan babban lauyan wanda ake ƙara bai samu halartar kotu ba sakamakon rashin lafiya.

Ana tuhumar nas ɗin ne da laifin haddasa mutuwa yayin aikata wani laifi ƙarƙashin dokar Penal Code ta jihar Kebbi.

A cewar masu gabatar da ƙara, lamarin ya faru ne a watan Maris lokacin da ake kula da Zulaihat Sale mai shekara bakwai da kuma Mufida Sale mai shekara uku a asibitin.

Gwamnatin jihar ta yi zargin cewa nas ɗin ta yi amfani da allurar quinine ta hanyar da ba ta dace ba, wanda ake zargin ya sa yaran suka suma kafin daga bisani su rasu.

Lauyoyin gwamnati ba su yi adawa da buƙatar ɗage shari’ar ba, amma sun roƙi ɓangaren kariya su kasance cikin shiri a zaman kotu na gaba domin shaidun sun yi tafiya daga Zuru zuwa Birnin Kebbi domin sauraron karar.

More from this stream

Recomended