Kasuwar ‘yan ƙwallo: Makomar Zaha da Costa da Ramos da Isco

Sergio Ramos

Koin Tottenham Hotspur Jose Mourinho na fatan sake haɗuwa da Sergio Ramos yayin da yake bin sahun tattaunawar kwantaragin ɗan wasan mai shekara 34 a Real Madrid. (Evening Standard via Mail)

AC Milan na son ɗaukar Wilfred Zaha na Crystal Palace a watan Janairu kuma tana ganin ɗan ƙasar Ivory Coast ɗin mai shekara 28 zai taimaka mata ɗaukar kofin Serie A na farko cikin shekara 10. (Sun)

Haka nan, Milan ɗin na da ƙwarin gwiwar cewa mai tsaron ragarta, Gianluigi Donnarumma mai shekara 21, zai ci gaba da zama a ƙungiyar. (Corriere Della Sera)

Ɗan wasan gaba na Atletico Madrid da Spain, Deigo Costa mai shekara 32, ya nemi ƙungiyar ta soke kwantaraginsa tare da barinta a watan Janairu. (Goal)

Sai dai Arsenal na yunƙurin ɗaukar Costa ɗin saboda tana son ƙara sayen ɗan wasan gaba. (AS via Express)

Idan ƙungiyoyin Real Madrid ko Barcelona ko Sevilla suna son sayen Diego Costa sai sun biya fan miliyan 22.7. (El Mundo)

Tsohon kocin PSG da aka kora, Thomas Tuchel, na cikin jerin waɗanda za su maye Frank Lamprad a Chelsea, wanda ake ƙara matsa wa lamba. (Bild via Eurosport)

Ana kyautata zaton ɗan wasan tsakiyar Real Madrid da Spain, Isco, zai koma gasar Premier League sama da Serie A, yayin da Arsenal da Everton ke ƙoƙarin ɗaukarsa. (Mundo Deportivo)

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa ɗaya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faɗa tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...