Kasuwar cinikin ‘yan ƙwallon ƙafa: Makomar Pogba, Tomori, Sanches, Wijnaldum, Williams, Giroud

Paul Pogba

Juventus ta soma tattaunawa da wakilin Paul Pogba Mino Raiola a yayin da take yunkurin sake daukar dan wasan na Manchester United mai shekara 27. (Express)

Dan wasan Chelsea da Ingila Fikayo Tomori, mai shekara 22, wanda ake rade radin zai tafi Leeds, na shirin tafiya kungiyar kwallon kafar Rennes da ke Faransa domin yin zaman aro zuwa karshen kakar wasa ta bana. (Talksport)

Liverpool ta mayar da hankali kan Sanches ne domin ya maye gurbin Georginio Wijnaldum, wandatake son rikewa, ko da yake ba ta son amincewa da bukatar dan wasan mai shekara 30 dan kasar Netherlands ta ba shi kwangilar shekara hudu. (Express)

Manchester United za ta jira zuwa watan Janairu domin yanke hukunci kan ko za ta bar dan wasan Ingila mai shekara 20 Brandon Williams – wanda ake rade radin zai tafi Southampton ko Newcastle – ya tafi zaman aro. (Manchester Evening News)

Chelsea na da kwarin gwiwar rike Olivier Giroud a watan Janairu kuma ta ci gaba da nuna wa dan wasan mai shekara 34 cewa zai buga tamala sosai domin ya zauna a gurbinsa a tawagar Faransa yadda zai samu damar buga gasar European Championships a bazara mai zuwa. (Telegraph – subscription required)

Dan wasan Paris St-Germain Neymar ya yi watsi da rade radin da ake yi cewa zai koma Barcelona, inda dan wasan na Brazil mai shekara 28 ya dage cewa yana zaue cikin farin ciki a PSG. (Express)

Arsenal tana iya yunkurin daukar dan wasan Porto dan kasar Portugal Fabio Vieira a watan Janairu kuma a shirye take ta biya kudin darajar dan wasa da suka kai £27m. (Record, via Mail)

Manchester United ta farfado da sha’awarta ta daukar dan wasan Atletico Madrid da Sifaniya Saul Niguez, mai shekara 26. (Todo Fichajes, via Team Talk)

Kocin Arsenal Mikel Arteta ya bukaci kungiyar ta dauko dan wasan Real Madrid dan kasar Sifaniya Isco, mai shekara 28, da dan wasan Lyon dan kasar Faransa Houssem Aouar, mai shekara 22, a watan Janairu. (Defensa Central, via Team Talk)

David Moyes yana zumudin inganta tawagar West Ham a watan Janairu amma ya gargadi magoya bayan kungiyar da kada su yi tsammanin zai sayi “manyan ‘yan wasa”. (London Evening Standard)

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa ɗaya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faɗa tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...