Kasashen Musulmi sun yi tir da ƙona Alkur’ani a Sweden

Kasashen Musulmin duniya na ci gaba da yin tir da kona Alƙur’ani da masu fitowa zanga-zanga suka yi a kasar Sweden.

Kasar Maroko da ke Afirka ta yi wa jakadanta na can kiranye, sakamakon lamarin da ya faru

Wannan lamari dai ya faru ne a birnin Stockholm.

Ma’aikatar harkokin wajen kasar a birnin Rabat ta kira matakin a matsayin rashin da’a ga al’ummar musulmi, yayin da suke bikin Babbar Sallah.

Ministan harkokin wajen Turkiyya ya yi Allah-wadai da lamarin, inda ya ce wadanda suka shiya zanga-zangar na da hannu a abun da ya faru.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]