Kasashen Musulmi sun yi tir da ƙona Alkur’ani a Sweden

Kasashen Musulmin duniya na ci gaba da yin tir da kona Alƙur’ani da masu fitowa zanga-zanga suka yi a kasar Sweden.

Kasar Maroko da ke Afirka ta yi wa jakadanta na can kiranye, sakamakon lamarin da ya faru

Wannan lamari dai ya faru ne a birnin Stockholm.

Ma’aikatar harkokin wajen kasar a birnin Rabat ta kira matakin a matsayin rashin da’a ga al’ummar musulmi, yayin da suke bikin Babbar Sallah.

Ministan harkokin wajen Turkiyya ya yi Allah-wadai da lamarin, inda ya ce wadanda suka shiya zanga-zangar na da hannu a abun da ya faru.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]