Jami’ar Abuja Ta Kori Dalibai 28 Kan Laifuka Daban-daban

University of Abuja (wadda yanzu ake kira Yakubu Gowon University) ta kori dalibai 28 bisa laifuka da suka hada da satar jarrabawa, amfani da kwayoyi da sauran manyan laifuka.

Hukuncin ya fito ne bayan taron majalisar jami’ar karo na 191, inda aka duba rahoton kwamitin ladabtar da dalibai.


Majalisar jami’ar ta kuma amince da janye takardun shaidar kammala karatu daga tsofaffin dalibai 15 da suka ki amsa gayyatar kwamitin ladabtarwa sau da dama.

Bugu da kari, an wanke dalibai tara daga zargi bayan bincike. Wasu dalibai 33 sun samu gargadi kan laifuka kamar damfara a dakunan kwana, hada baki da kuma fada.

Da yake martani, mataimakin shugaban jami’ar, Hakeem Fawehinmi, ya ce jami’ar ba za ta lamunci duk wani abu da zai lalata mutuncin ilimi ko kuma tsaron harabar makaranta ba.

Ya kara da cewa jami’ar na kokarin samar da muhalli mai kyau da aminci ga dalibai da ma’aikata.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]