Iran Ta Ce An Samu Gagarumin Ci Gaba A Tattaunawa Da Amurka



Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi, ya bayyana cewa an samu babban ci gaba a tattaunawar da ƙasarsa ke yi da Amurka a Switzerland.

Araghchi ya ce an sassauta wasu takunkuman da aka sanya wa Iran kan fitar da man fetur da kayan petrochemical, sannan an dakatar da wasu matakan hana ruwa da aka kakaba wa ƙasar.

A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, ministan ya ce an kuma saki wasu kadarorin Iran da aka ƙwace a ƙasashen waje tare da fara aiwatar da shirin farfaɗo da tattalin arzikin ƙasar.

Ya gode wa ƙasashen Pakistan da Qatar bisa rawar da suka taka wajen shiga tsakani, yana mai cewa hakan ya taimaka wajen ƙoƙarin kawo ƙarshen rikicin Lebanon.

Araghchi ya ƙara da cewa daga cikin matakan da aka amince da su akwai kafa wata hanya ta musamman domin tabbatar da dakatar da faɗa a Lebanon.

Ya ce har yanzu ana ci gaba da tattaunawa tsakanin Iran da Amurka domin cimma yarjejeniya ta ƙarshe kan batutuwan da suka haɗa da tsagaita yaƙi, sassauta takunkumi da kuma sakin kadarorin Iran da aka ƙwace.

More from this stream

Recomended