IGP Disu Ya Gargadi ’Yan Sanda Kan Bidiyo Ko Rubutu a Social Media



Sufeto Janar na ’Yan Sandan Najeriya, Tunji Disu, ya gargadi jami’an rundunar da su guji gudanar da ayyukan kafafen sada zumunta ba tare da izini ba yayin da suke cikin kayan aikin ’yan sanda.

Kakakin rundunar, Anietie Edem, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da aka fitar ranar Talata.

Sanarwar ta ce an dauki matakin ne bayan karuwar jami’an da ke wallafa bidiyo, gudanar da shirin kai tsaye da kuma yin sharhi kan harkokin rundunar a shafukan sada zumunta ba tare da sahalewar hukuma ba.

A cewar sanarwar, an hana jami’ai wallafa bayanai ko hotuna cikin kayan aiki tare da yin magana kan al’amuran rundunar ba tare da izini ba. Haka kuma an gargade su da kada su bayyana bayanan sirri na ayyukan tsaro ko amfani da mukamansu domin talla, nishaɗi ko neman suna.

Sanarwar ta ambato cewa, “The Inspector-General of Police, IGP Olatunji Rilwan Disu, psc(+), NPM, has directed all officers and men of the Nigeria Police Force to desist from unauthorised social media activities capable of undermining the integrity, professionalism, and public image of the Force.”

Disu ya kuma umarci kwamishinonin ’yan sanda da sauran manyan jami’ai su fadakar da jami’an da ke karkashinsu tare da tabbatar da bin dokar.

Haka kuma ya umarci sashen leƙen asiri da na ladabtarwa na rundunar su tsaurara sa ido kan ayyukan jami’an a kafafen sada zumunta.

More from this stream

Recomended