Rundunar Hisba da ke Azare a ƙaramar hukumar Katagum ta jihar Bauchi ta tabbatar da kama wasu mutum bakwai da ake zargi da musayar matansu na aure a tsakaninsu.
Kwamandan Hisba a yankin, Malam Ridwan Muhammad Khairan, ya shaida wa BBC cewa an kama mutanen ne bisa zargin aikata wani abu da ya bayyana a matsayin laifi wanda ba a saba ji ko ganin irinsa ba.
Ya ce abin da ake zargin mutanen sun aikata ya saɓa da koyarwar addinin Musulunci, wanda ya tanadi mace ta kasance ƙarƙashin aure da namiji guda kawai.
Wasu masu sharhi kan al’amuran yau da kullum a jihar Bauchi sun yaba da matakin da Hisba ta ɗauka na gudanar da samame da kama waɗanda ake zargin. Sun ce idan aka yi shiru kan irin wannan lamari, akwai yiwuwar ya bazu cikin al’umma.
Hisba Ta Kama Mutum Bakwai Kan Zargin Musayar Matansu A Bauchi

