Gwamnatin Tarayya Ta Karɓi Rahoton Bincike Kan Zargin Cin Hanci Da Azabtarwa a Gidajen Gyaran Hali



Gwamnatin Tarayya ta karɓi rahoton kwamitin bincike mai zaman kansa da ya gudanar da bincike kan zarge-zargen cin hanci, azabtarwa, amfani da iko ba daidai ba da sauran laifuka a gidajen gyaran hali na Najeriya.

Ministan Harkokin Cikin Gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, ya bayyana hakan, inda ya ce an kafa kwamitin ne a watan Nuwamban shekarar dubu biyu da ashirin da huɗu, kuma ya kammala aikinsa bayan watanni goma sha takwas na bincike.

Ministan ya ce rahoton zai zama jagora wajen aiwatar da sauye-sauye domin mayar da gidajen gyaran hali cibiyoyin gyaran tarbiyya da sake shigar da fursunoni cikin al’umma.

Ya kuma bayyana cewa yawan tsofaffin fursunonin da suka koma gidan yari bayan sake su ya ragu daga mutum dubu goma sha ɗaya da ɗari shida da goma sha shida a shekarar dubu biyu da ashirin da uku zuwa mutum dubu ɗaya da ɗari uku da tamanin da biyu a shekarar dubu biyu da ashirin da biyar.

A cewarsa, fursunoni sittin da biyu na karatun digiri na biyu, yayin da ɗari biyu da sittin da ɗaya ke karatun digiri. Haka kuma, mutum dubu ɗaya da ɗari ɗaya da ashirin da biyar na cikin shirye-shiryen ilimi, yayin da mutum dubu tara da ɗari biyar da tamanin da biyu ke koyon sana’o’i daban-daban.

Tunji-Ojo ya jaddada kudirin gwamnati na tabbatar da adalci da mutunta ɗan Adam a gidajen gyaran hali, tare da aiwatar da shawarwarin da ke cikin rahoton domin inganta tsarin gudanar da su a faɗin ƙasar nan.

More from this stream

Recomended