Gwamnan Nasarawa Zai Nemi Kujerar Sanata A 2027

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar sanatan Nasarawa ta Arewa a zaɓen shekarar 2027.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa gwamnan ya bayyana hakan ne yayin da majalisar zartaswar jihar ta kai masa ziyarar barka da sallah a gidansa da ke unguwar Gudi, a ƙaramar hukumar Akwanga.

Gwamna Sule ya ce sarakunan gargajiya da manyan ’yan siyasar yankin Nasarawa ta Arewa ne suka matsa masa da kiraye-kirayen ya tsaya takarar.

A cewarsa, “La’akari da matsin na nake samu daga jagororinmu, kuma ba na son su ga kamar na ƙi yi musu abin da suke so, na yi alƙawarin tsayawa takarar idan lokacin ya zo.”

Ya kuma ƙara da cewa a baya ya yi niyyar goyon bayan wani ɗan takara, amma daga bisani ya sauya shawara bayan da mutumin ma ya shiga cikin masu kiraye-kirayen ya fito takarar.

Wannan mataki na gwamnan na nuni da yadda harkokin siyasa ke fara ɗaukar zafi gabanin zaɓen 2027 a jihar.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]