Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umaru Raɗɗa, ya biya wa maniyyatan jihar kuɗin hadaya domin sauƙaƙa musu gudanar da aikin Hajjin bana.
An bai wa kowane maniyyaci Riyal 500 na Saudiyya a matsayin kuɗin hadaya, bayan gwamnatin jihar ta bayyana cewa dala 500 da aka ware musu a matsayin guzuri ba za su wadace su ba.
Babban Daraktan Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta jihar, Alhaji Yunusa Abdullahi Dankama, ya ce gwamnatin Katsina ta kashe sama da naira biliyan uku wajen shirye-shiryen aikin Hajjin bana da kuma tabbatar da samun kujerun maniyyata 2,035 ga jihar.
Gwamna Raɗɗa ya kuma ce gwamnatin jihar ta ɗauki nauyin malamai, jami’an lafiya da sauran ma’aikatan da za su taimaka wa maniyyata a ƙasa mai tsarki.
Ana sa ran fara jigilar maniyyatan shiyyar Funtua zuwa Saudiyya a ranar Litinin mai zuwa.
Gwamnan Katsina Ya Biya Wa Maniyyatan Jiharsa Kuɗin Hadaya

