Gwamnan Edo Zai Fara Biyan 70,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki ya sanar da mafi ƙarancin albashi ga ma’aikatan ga ma’aikatan jihar inda za a riƙa biyan naira dubu 70,000.

Gwamnan ya sanar da haka a ranar Litinin a wurin bikin buɗe ginin sabon ginin da ake Kira Gidan Ƴan Kwadago.

Obaseki ya ce gidan na ƴan ƙwadago za a riƙa kiransa da sunan tsohon gwamnan jihar, Kwamared Adam Oshiomhole.

Sabon mafi ƙarancin albashin zai fara ne daga ranar 1 ga watan Mayun 2024 a a cewar gwamnan .

Kungiyoyin kwadago na TUC da NLC sun jima suna fafutukar ganin an yi ƙarin albashi ga ma’aikata duba da yadda aka samu hauhuwar farashin kayayyaki da kuma cire tallafin man fetur da aka yi.

More News

Peter Obi Ya Ziyarci Mutanen Da Su Ka Ƙone Sakamakon Wutar Da Wani Ya Cinnawa   Masallaci A Kano

Ɗan takarar shugaban ƙasa  a zaɓen 2023 ƙarƙashin jam'iyar Labour Party (LP) Peter Obi ya ziyarci mutanen da wani matashi ya cinnawa wuta a...

An sanar da zaman makoki na kwana biyar saboda mutuwar shugaban kasa a Iran

Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya sanar da zaman makoki na kwanaki biyar saboda rasuwar shugaban kasar Ibrahim Raisi...

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa ɗaya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...