Guguwar Iska Ta Lalata Kusan Gidaje 100 A Jihar Filato


Wata guguwar iska da ta biyo bayan ruwan sama mai ƙarfi ta lalata kusan gidaje 100 a ƙauyen Tom Gangare da ke gundumar Sopp a ƙaramar hukumar Riyom ta Jihar Filato.

Rahotanni sun ce guguwar, wadda ta afku a ranar Lahadi, ta kuma lalata cibiyoyin lafiya, wuraren ibada da sauran kayayyakin more rayuwa, lamarin da ya tilasta wa iyalai da dama barin gidajensu.

Wani mazaunin yankin, Bot Felix, ya ce iska mai ƙarfi ta tumbuke bishiyoyi da dama, inda wasu daga cikinsu suka faɗa kan gidaje, abin da ya ƙara tsananta asarar da aka yi.

Shugaban al’umma, Dung Danboyi, ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici tare da yin kira ga hukumomin gwamnati da ƙungiyoyin agaji su kai ɗauki ga waɗanda abin ya shafa.

A nasa ɓangaren, shugaban ƙaramar hukumar Riyom, Sati Bature Shuwa, ya ziyarci yankin domin duba irin barnar da aka yi tare da jajanta wa mazauna yankin. Ya kuma tabbatar da cewa za a gudanar da cikakken bincike kan asarar da aka yi domin samar da tallafin da ya dace ga waɗanda abin ya shafa.

More from this stream

Recomended