Firimiya: ‘Yan wasan Arsenal za su gudu saboda Emery

Emery

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Shuwagabannin kulob din Arsenal sun ce za a sha wahala kafin a iya shawon kan manyan ‘yan wasan kungiyar, matsawar Unai Emery ya ci gaba da jan ragamarta. (Mail)

Raheem Sterling na Manchester City na jiran ya ga idan har mai horar da ‘yan wasa Pep Guardiola zai ci gaba da zama da kungiyar kafin ya iya saka hannu kan sabuwar yarjejeniya. (FourFourTwo)

A wata mai kama da haka, Guardiola ya ce kungiyoyin da ke tunanin kulla yarjejeniya da mai taimaka masa Mikel Arteta irinsu Arsenal da Everton, sun kwana da shirin cewa ba zai bar kungiyar ba a kalla sai zuwa karshen kakar wasannin bana. (Times)

Jose Mourinho na Tottenham na duba yiwuwar sayen mai tsaron bayan Benfica Ruben Dias mai shekaru 22, da kuma dan wasan tsakiyar Sporting Lisbon Bruno Feranades mai shekaru 25. (90min)

West Ham ma tunanin kawo mai horar da ‘yan wasan Shefield United Chris Wilder, idan har sun yanke shawarar sallamar Manuel Pellegrini. (Mirror)

Rahotanni sun ce an argadi Pellegrini kan cewa dole ne abubuwa su sauya, a wata tattauna wa da shugabannin kungiyar. (Talksport)

Ejan din mai tsaron bayan Manchester United Chris Smalling, ya isa Italiya don fara tattauna wa da kulob din AS Roma kan yiwuwar kulla yarjejeniyar ta din-din-din da kungiyar, bayan kammala zaman aro da yake yi.

More News

Peter Obi Ya Ziyarci Mutanen Da Su Ka Ƙone Sakamakon Wutar Da Wani Ya Cinnawa   Masallaci A Kano

ÆŠan takarar shugaban Æ™asa  a zaÉ“en 2023 Æ™arÆ™ashin jam'iyar Labour Party (LP) Peter Obi ya ziyarci mutanen da wani matashi ya cinnawa wuta a...

An sanar da zaman makoki na kwana biyar saboda mutuwar shugaban kasa a Iran

Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya sanar da zaman makoki na kwanaki biyar saboda rasuwar shugaban kasar Ibrahim Raisi...

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa É—aya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...