A ranar Laraba ake sa ran Fafaroma Leo zai isa kasar Kamaru, a matsayin bangare na biyu na rangadin da yake yi a nahiyar Afirka.
Yayin ziyarar, Fafaroman zai gana da shugaban kasar, Paul Biya, wanda ake ganin shi ne shugaban kasa mafi tsufa a duniya, kuma ya shafe sama da shekaru 40 yana mulki.
A ranar Alhamis kuma, Fafaroma Leo zai kai ziyara birnin Bamenda, wanda ke zama cibiyar rikicin ‘yan a-ware masu neman ‘yancin yankin masu amfani da harshen Ingilishi a kasar.
Ana sa ran jagoran darikar Katolika ta duniya zai jagoranci addu’o’i tare da gabatar da muhimmin jawabi da zai mayar da hankali kan zaman lafiya da sasanci.
Tun bayan barkewar rikicin ‘yan a-ware a shekarar 2017, Cocin Katolika ta ci gaba da kira ga bangarorin da abin ya shafa da su rungumi tattaunawa domin warware rikicin cikin lumana.
Fafaroma Leo Zai Ziyarci Kamaru Domin Kiran Zaman Lafiya

