Egypt ta yi waje da Kamaru a gasar AFCON

‘Yan wasan Egypt sun samu nasarar cire I kasar Kamaru da ke karbar bakuncin gasar cin kofin kasashen nahiyar Afirka a gasar ta AFCON.

Hakan na nufin kasar ta Masar ta kai wasan karshe.

Egypt ta yi nasara ne da bugun fenariti da ci 3-1 bayan da aka kwashe minti 120 babu wanda ya zura kwallo.

Yanzu ‘yan wasan na Masar za su hadu da Senegal wacce tuni ta kai zagayen wasan karshe.

‘Yan wasan Kamaru sun zubar da fenariti uku a bugun daga kai sai mai tsaron gidan yayin da Egypt kuma ta ci duka wadanda ta buga.

Yanzu Kamaru za ta hadu da Burkina Faso don neman matsayi na uku a gasar ta AFCON wacce ake yi a karo 33.

Bangarorin biyu sun yi ta fafatawa cikin zagayen farko da kuma bayan an dawo daga hutun rabin lokaci, amma babu wanda ya kai ga gaci ta hanyar cin kwallo.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon ɗaya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...