DSS ta sake kama wani dan ta’adda da ya tsere daga gidan yarin Kuje

Hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta samu nasarar sake kama, Abdulazeez  Obadaki wani dan ta’adda da ake nema ruwa a jallo kuma ɗaya daga cikin daurarrun da suka tsere daga gidan yarin Kuje a shekarar 2022.

Daurarru sama da 800 ne cikin har da wadanda yan kungiyar Boko Haram ne suka tsere daga gidan yarin lokacin da wasu yan bindiga dauke da makamai suka kai farmaki gidan yarin.

Obadaki ne ya shirya kai hari kan wasu bankunan kasuwanci dake gari Uromi na jihar Edo da kuma harin da aka kai Deeper Life College dake garin Okene ta jihar Kogi a shekarar 2022.

Wata majiya dake hukumar ta DSS ta bayyana cewa, Obadaki wanda mamba ne na kungiyar yan ta’adda ta Ansaru an kama shi ne da safiyar ranar Juma’a.

A cikin watan Agusta ne mai bawa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu ya sanar da kama biyu daga cikin wadanda suke jagorantar ƙungiyar ta Ansaru da ake zargi da shirya kai harin gidan yarin na Kuje.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]