Dimokradiyya: Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin 12 ga wata a matsayin ranar hutu

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Litinin 12 ga watan Yunin 2023 a matsayin ranar hutu domin tunawa da ranar dimokuradiyya ta bana.

Dokta Oluwatoyin Akinlade ne ya bayyana hakan a madadin gwamnatin tarayya, inda ya taya daukacin ‘yan Nijeriya murnar wannan rana.

“Tafiyar Dimokuradiyyar Najeriya, kamar a sauran yanayi da dama, ta ci karo da kalubale, amma shugabannin kasa, da cibiyoyinta da ma al’ummar Nijeriya, sun tsaya tsayin daka kan tsarin mulkin dimokradiyya.

“Saboda haka, a wannan karon, an gayyaci ‘yan Nijeriya da abokan Nijeriya, da su yaba irin ci gaban da aka samu, da nuna farin cikinsu, da kuma fatan samun kyakkyawar makoma ga dimokuradiyyar kasar nan,” inji shi.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]