Dimokradiyya: Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin 12 ga wata a matsayin ranar hutu

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranar Litinin 12 ga watan Yunin 2023 a matsayin ranar hutu domin tunawa da ranar dimokuradiyya ta bana.

Dokta Oluwatoyin Akinlade ne ya bayyana hakan a madadin gwamnatin tarayya, inda ya taya daukacin ‘yan Nijeriya murnar wannan rana.

“Tafiyar Dimokuradiyyar Najeriya, kamar a sauran yanayi da dama, ta ci karo da kalubale, amma shugabannin kasa, da cibiyoyinta da ma al’ummar Nijeriya, sun tsaya tsayin daka kan tsarin mulkin dimokradiyya.

“Saboda haka, a wannan karon, an gayyaci ‘yan Nijeriya da abokan Nijeriya, da su yaba irin ci gaban da aka samu, da nuna farin cikinsu, da kuma fatan samun kyakkyawar makoma ga dimokuradiyyar kasar nan,” inji shi.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...