Dan Najeriya Ya Mutu A Kogin London Yayin Ceto Wata Mata

Ruwa ya ci wani dan asalin Najeriya mai shekara 20 yayin da yake kokarin ceto wata mata da ta fada Kogin Thames da ya ratsa birnin London a Ingila.

Jaridun Birtaniya da dama sun ruwaito cewa Folajimi Olubunmi-Adewale ya fanjama cikin kogin ne bayan da hango matar ta fada cikinsa.

Lamarin ya faru ne da misalin karfe 12 na daren ranar Asabar.

Bayanai sun yi nuni da cewa wani mutum na biyu, wanda shi ma ya ga fadawar matar, ya shiga kogin domin ya ceto ta.

Jami’an ba da agajin gaggawa sun garzaya kogin a lokacin da aka sanar da su, inda daga baya suka ceto matar da wani mutum daban, amma ba su ga Olubunmi-Adewale ba.

Rahotanni sun ce sai da misalin karfe 6 na safe aka ga gawar wani mutum, wacce daga baya aka ayyana a matsayin ta Olubunmi-Adewale ce.

“Folajimi Olubunmi-Adewale ya fi kowa a cikinmu. Jarumi ne na kwarai a wannan birni namu, wanda ya sadaukar da rayuwarsa domin ceto wani ran. Tunanina da addu’o’ina na tare iyalansa da abokansa a wannan lokaci na alhini.” Magajin birnin London Sadiq Khan ya rubuta a shafinsa na Twitter.

Shaidu sun ce igiyar ruwan kogin na Thames da ke kadawa a lokacin na da karfin gaske, abin da ake ganin ya sa matashin ya gaza cimma burinsa.

Jama’a da dama a kasar ta Birtaniya, sun jijinawa Olubunmi-Adewale bisa wannan namajin yunkuri da ya yi.

Thames, kogi ne da ya ratsa ta yankin kudancin Ingila da ya hada da birnin London.

Shi ne kogi mafi tsawo a daukacin Ingila kuma na biyu a tsawo a daukacin kasar ta Birtaniya baya ga Kogin Severn da ya kasance na farko.

More News

Najeriya za ta dena shigo da man fetur a cikin watan Yuni – Dangote

Aliko Dangote mutumin da ya fi kowa arziki a Nahiyar Afirka ya ce Najeriya za ta daina shigo da man fetur a cikin watan...

An ceto mutane 9 daga wani ginin bene da ya ruguzo a jihar Niger

Mutane 9 aka samu nasarar cetowa daga wani ginin bene mai hawa É—aya da ya ruguzo a yankin Sabon Gwari dake garin Minna babban...

An yi faÉ—a tsakanin masu sayar da waya da sojoji a kasuwar Abuja

Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya, ta tura jami’an leken asiri zuwa kasuwar Banex – wata kasuwar kayan lantarki da na’urorin sadarwa da ke...

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...